





























Hadeeth Cards
Da'wa cards that highlight great meanings from the noble prophetic hadiths in a simple style and attractive display that helps the Muslim to have a deeper understanding of his religion in an easy way
All
Daga Abu Musa Al-ash'ariy Allah Ya yarda da shi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Ku dinga maimaita wannan Alƙur’anin, ina rantse muku da wanda ran Muhammad yake a hannunSa ya fi saurin kufcewa sama da raƙumin da ya ke a dabaibayi.
Bukhari da Muslim suka Rawaito shiAnnabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi umarnin yawan maimaita Alƙur’ani da dagewa a kan karanta shi; domin kada a manta bayan an haddace shi a zuciya, [Annabi] tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kuma ƙarfafi hakan da rantsuwa a kan Alƙur’ani ya fi saurin ɓacewa da tafiya daga zuciya a kan raƙumi da aka ɗaure, ga shi a ɗaure da igiya a ƙwauri, idan mutum yana yawan bibiyarsa sai ya riƙeshi, idan kuma ya sakeshi sai ya tafi ya ɓace.
Daga Usman Allah Ya yarda da shi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi ya ce: "Mafi alherinku shi ne wanda ya koyi Alkur’ani kuma ya koyar da shi".
Buhari ne ya rawaito shiAnnabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana ba da labarin mafi falalar Musulmai, wanda kuma yake ƙololuwar daraja a wurin Allah shi ne, wanda ya koyi Alƙur’ani, karatun da hadda da rerawa da fahimta da Tafsir. Ya kuma sanar da wani abin da yake wurinsa na iliman Alkur’ani (Ulumul Qur’an) tare da aiki da shi.
Daga Abu Hurairah Allah Ya yarda da shi, Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Kada ku mayar da gidajenku makabarta, Shaiɗan yana guduwa daga gidan da ake karanta Surat Al-Bakarah a cikinsa".
Muslim ne ya rawaito shiAnnabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana yin hani daga wofintar da gidaje daga sallah, sai su zama kamar maƙabartu, da ba a sallah a cikinsu. Sannan sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba da labarin shaiɗan yana ficewa daga gidan da ake karanta Suratul Baƙara.
Daga Abu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: Wanda ya karanta ayoyi biyu na ƙarshen Suratul Bakara da daddare sun ishe shi.
Bukhari da Muslim suka Rawaito shiAnnabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba da bayanin duk wanda ya karanta ayoyi biyun ƙarshe na Suratul Baƙara cikin dare, to, Allah zai tsare shi daga sharri da abin ƙi, wasu kuma suka ce: Sun ishe shi nafilar dare, wasu kuma suka ce: Sun ishe shi addu’oin dare. An ce kuma: su ne mafi ƙarancin abin da zai isa na karatun Alkur’ani a nafilar dare, an ma faɗi wanin haka, kuma muna fatan duk abin da aka faɗa ɗin daidai ne, domin zai ƙunshe su duka
An karbo daga Abdullahi Ɗan Mas’ud Allah ya yarda da shi ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Duk wanda ya karanta wani harafi daga littafin Allah, to, yana da lada, kuma kowane lada za a ninkashi goma. amma ba zan ce Alif Laam Meem harafi ɗaya ba ne, sai dai Alif, harafi ne, Laam harafi ne, Meem harafi ne"
Al-Tirmithi Ya Rawaito shiAnnabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba da labari cewa kowanne Musulmi ne ya karanta harafi daga littafin Allah, to, yana da lada a wannan karatun, kuma za a ninka masa lada zuwa ninki goma. Sannan ya yi bayanin hakan da faɗinsa: Ban ce : Alif, Laam, Meem, harafi ba ne, sai dai Alifun harafi ne, Lamun harafi ne, Mimun harafi ne, sai ya kasance harufa uku, lada talatin kenan.
Daga Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana ambaton Allah a kodayaushe.
Bukhari Ya Rawaito shi Mu'allak amma ta Sigar YankewaNana A'isha uwar Muminai Allah Ya yarda da ita, tana ba da bayanin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana tsananin kwaɗayi a kan yin ambaton Allah maɗaukaki, kuma ya kasance yana ambaton Allah a kowanne lokaci da kowanne yanayi.
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa: "Allah - maɗaukakin sarki Ya ce: Na raba sallah tsakanina da tsakanin bawaNa gida biyu, bawaNa yana da abin da ya roƙa, idan bawa ya ce: {Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai}, Allah - Maɗaukakin sarki - zai ce: bawaNa ya godemin, idan ya ce: {Mai kyauta a duniya mai jin ƙan muminai a lahira}, Allah - Maɗaukakin sarki - zai ce: BawaNa ya yabeni, idan ya ce: {Mamallakin ranar sakayya}, Zai ce: BawaNa ya girmamaNi, - wani lokaci kuma ya ce: bawaNa ya fawwala (al'amuransa) gareNi -, idan ya ce: {Kai kaɗai muke bautawa, kuma gareka kaɗai muke neman taimako}, sai Ya ce: Wannan tsakanina da tsakanin bawaNa ne, kuma bawaNa yana da abin da ya roƙa, idan ya ce: {ka shiryar da mu hanya madaidaiciya, hanyar waɗanda Ka yi ni'ima a garesu ba waɗanda Ka yi fushi a kansu ba, ba kuma ɓatattu ba}, zai ce: Wannan ga bawaNa ne, kuma bawaNa yana da abin da ya roƙa".
Muslim ne ya rawaito shiAnnabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ba da labarin cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa a hadisi Qudsi: Na raba Surar fatiha a sallah gida biyu tsakanina da tsakanin bawaNa, rabinta nawa ne, rabinta kuma nasane. Rabinta na farko: Godiya ne da yabo da girmama Allah, zan saka masa da mafificin sakamako. Rabinta na biyu: Ƙanƙar da kai ne da addu'a, zan amsa masa, kuma zan ba shi abin da ya roƙa. Idan mai sallah ya ce: {Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai}, Allah zai ce: BawaNa ya gode min, idan ya ce; {Mai kyauta a duniya Mai jin ƙan muminai a lahira}, Allah zai ce: BawaNa ya yabeni, sai ya yabeNi ya yi iƙirari da gamewar baiwa ga halittata, idan ya ce: {Mamallakin ranar sakamako}, Allah zai ce: BawaNa ya girmamaNi, ita ce ɗaukaka mayalwaciya. Idan ya ce: {Kai kaɗai muke bautawa, kuma gareka ne kaɗai muke neman taimako}, Allah zai ce: Wannan tsakanina ne da tsakanin bawaNa. Ɓangare na farko daga wannan ayar shi ne: {Kai kaɗai muke bautawa} shi ne iƙirari da Allantakar Allah, da kuma amsawa ga yin bauta, da shi ne ɓangaren da yake ga Allah ya kare. Ɓangare na biyu daga ayar shi ga bawa ne: {Gareka ne kaɗai muke neman taimako} neman taimako daga Allah ne, da kuma alƙawarinSa na taimako. Idan ya ce: {Ka shiryar da mu hanya madaidaiciya* Hanyar waɗanda Ka yi ni'ima garesu, ba waɗanda Ka yi fushi da su ba, ba kuma ɓatattu ba}, Allah zai ce: Wannan ƙanƙar da kai ne da addu'a daga bawaNa, kuma bawaNa yana da abin da ya roƙa, haƙiƙa na amsa addu'arsa.
Daga Sa'id Dan Musayyib daga babansa ya ce: Lokacin da mutuwa ta zo wa Abu Dalib, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zo masa sai ya samu Abu jahal da Abdullahi Dan Abu Umayyah Dan Mugira a wurrinsa, sai ya ce: "Ya kai baffana, ka ce : Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kalma ce wacce zan kafa maka hujja da ita awurin Allah", sai Abu jahal da Abdullahi dan Abu Umayyah suka ce : Kana kin tafarkin Abdul Muddalib, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai gushe ba yana bijiro masa da ita, suma suna maimaita masa waccan maganar, har Abu Dalib ya ce karshen abinda ya fada musu: Akan tafarkin Abdul Muddalib ya ki fadar: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah. Ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wallahi zan nemamaka gafara muddin ba'a hanani ba". Sai Allah yaYa saukar da: {Bai kasance ga Annabi ba da wadanda suka yi imani da su nema wa mushrikai gafara ba} [Al-Taubah: 113], kuma Alllah Ya saukar asha'anin Abu Dalib, sai Ya cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: {Lallai kai ba zaka shiryar da wanda kake so ba sai dai Allah Yana shiryar da wanda Ya so} [Al-Kasas: 56].
Bukhari da Muslim suka Rawaito shiAnnabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shiga wurin baffansa Abu Dalib alhali shi yana kan gargara, sai ya ce masa: Ya baffana, ka ce : "Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, wata kalmace da zan yi maka shaida da ita a wurin Allah, sai Abu Jahal da Abdullahi Dan Abu Umayya suka ce: Ya Abu Dalib, zaka bar tafarkin babanka Abdul Muddalib?! Shi ne bautar gumaka, basu gushe ba suna yi masa magana har ya fadi karshen wani abinda ya zantar da su da shi: Akan tafarkin Abdul Muddalib, tafarkin shirka da bautar gumaka, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Zan roka maka gafara muddin Ubangijina bai hanani hakan ba, sai fadin Allah - Madaukakin sarki - ya sauka: {Bã ya kasancẽwa ga Annabi da waɗanda suka yi ĩmãni, su yi istigifãri ga mushirikai, kuma kõ dã sun kasance ma'abũta zumunta ne daga bãyan sun bayyana a gare su, cẽwa lalle ne, sũ, 'yan Jahĩm ne} [Al-Taubah: 113], kuma fadin Allah - Madaukakin sarki - ya sauka a sha'anin Abu Dalib: {Lalle ne kai bã ka shiryar da wanda ka so, amma kuma Allah Yanã shiryar da wanda Yake so, kuma Shi ne Mafi sani daga mãsu shiryuwa} [Al-kasas: 56], lallai cewa kai ba ka shiryar da wanda ka so shiriyarsa, kawai kai isarwa ce taka, Allah Yana shiryar da wanda yake so.
Daga Abu Musa Al-Ash'ari - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Kwatankwacin muminin da yake karanta AlKur'ani kamar gawasa ne, kanshinta mai dadi ne, kuma dandanonta mai dadi ne, kuma kwatankwacin muminin da ba ya karanta AlKur'ani kamar dabino ne ba shi da kanshi amma dandanonsa ma zaki ne, kuma kwatankwacin munafikin da yake karanta AlKurani kamar nana ne kanshinsa mai dadi ne amma dandanonta mai daci ne, kuma kwatankawacin munafikin da ba ya karanta AlKura'ni kwatankwacin guna ce ba ta da kanshi, kuma dandanonta mai daci ne".
Bukhari da Muslim suka Rawaito shiAnnabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana karkasuwar mutane a karatun AlKur'ani da amfanuwa da shi: Kashi na farko: Muminin da yake karanta AlKur'ani kuma yake amfanuwa da shi, to shi kamar gawasa ne, mai dadin dandano da kanshi, da kyakkyawan launi, kuma amfaninsa mai yawa ne, shi yana aiki da abinda ya karanta, kuma yana amfanar bayin Allah. Kashi na biyu: Muminin da ba ya karanta AlKur'ani, to shi kamar dabino ne, dandanonsa mai zaki ne, kuma ba shi da kanshi, to zuciyarsa mai tattare da imani ce kamar tattarowar dabino akan zaki a dandanonsa da cikinsa, da rashin bayyanar kanshi gare shi wanda mutane za su shaka; Saboda rashin bayyanar karatu daga gare shi wanda mutane za su ji dadin jinsa. Na uku: Munafikin da yake karanta AlKur'ani: To shi kamar nana ne, tana da dadin kanshi kuma dandanonta mai daci ne, ta inda bai gyara zuciyarsa da imani ba, kuma bai yi aiki da AlKur'ani ba, kuma yana bayyana ga mutane cewa shi muminine, to kanshinta mai dadi yana kama da karatunsa, dandanonta mai daci kuma yana kama da kafircinsa. Na hudu: Munafikin da ba ya karanta AlKur'ani, to shi kamar guna ne, ta inda ita ba ta da kanshi, da kuma dacin dandanonta, to rashin kanshinta ya yi kama da rashin kanshinsa; Saboda rashin karatunsa, kuma dacin dandanonta ya yi kama da dacin kafircinsa, cikinsa ya kadaita daga imani, zahirinsa kuma babu amfani a cikinsa, kai shi mai cutarwa ne.